Matthew 21

1Yayinda Yesu da almajiransa suka kusato Urushalima sai suka zo Betafaji wajen dutsen zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa guda biyu, 2yace masu, “Ku shiga kauyen da yake gaban ku zaku iske wata jaka da aholaki tara da ita. Ku kwance su ku kawo mani su. 3Idan wani ya gaya maku wani abu game da haka, sai ku ce, ‘Ubangiji ne yake bukatarsu,’ mutumin kuwa zai aiko ku da su nan da nan.”

4Anyi wannan kuwa domin a cika annabcin anabin. Yace, 5“Ku cewa diyar Sihiyona, duba, ga sarkinki na zuwa wurin ki, mai tawali’u ne, kuma akan jaki wanda aholaki ne.”

6Sai almajiran suka tafi suka yi kamar yadda Yesu ya umarce su. 7Suka kawo jakar da dan aholakin, suka sa tufafinsu akai, Yesu kuwa ya zauna akan tufafin. 8Yawancin jama’a kuwa suka baza tufafinsu akan hanya, wasu kuma suka yanko ganye daga bishiyoyi suka shimfida su a hanya.

9Taron jama’a da suke gabansa da wadanda suke bayansa, suka ta da murya suna cewa, “Hossana ga dan Dauda! mai albarka ne shi wanda ke zuwa cikin sunan Ubangiji. Hossana ga Ubangiji!” 10Sa’adda Yesu ya shiga Urushalima sai doki ya cika birnin ana cewa, “Wanene wannan?” 11Sai jama’a suka amsa, “Wannan shine Yesu annabi, daga Nazaret ta Galili.”

12Sai Yesu ya shiga haikalin. Ya kori duk wadanda ke saye da sayarwa a cikin ikiilisiya. Ya birkice teburan masu canjin kudi da kujerun masu sayar da tantabaru. 13Ya ce masu, “A rubuce yake, ‘Za a kira gidana gidan addu‘a,’ amma kun mayar dashi kogon ‘yan fashi.” 14Sai makafi da guragu suka zo wurin sa a haikalin, ya warkar da su.

15Amma da manyan firistoci da malaman attaura suka ga abubuwan banmamaki da yayi, kuma sa’adda suka ji yara suna tada murya a cikin haikalin suna cewa, “Hossana ga dan Dauda,” sai suka ji haushi. 16Suka ce masa, kana jin abinda wadannan mutanen ke fadi?‘’ Yesu ya ce masu, “I! Amma ba ku taba karantawa ba, ‘daga bakin jarirai da masu shan mama ka sa yabo’?” 17Sai Yesu ya bar su, ya fice daga birnin zuwa Betaniya ya kwana a wurin.

18Washegari da safe yayin da yake komawa birnin, sai yaji yunwa. 19Da ya ga bishiyar baure a bakin hanya, sai yaje wurin amma bai sami kome ba sai dai ganye. Sai ya ce mata, “Kada ki kara yin ‘ya’ya har abada.” Sai nan take bishiyar bauren ta bushe.

20Da almajiran suka ga haka, sai suka yi mamaki suka ce, “Kaka bishiyar bauren ta bushe nan da nan?” 21Yesu ya amsa yace masu, “Hakika ina ce maku, in dai kuna da bangaskiya ba ku yi shakka ba, ba abinda aka yi wa bauren nan kadai za kuyi ba har ma za ku cewa tsaunin nan, “Ka ciru ka fada teku,’ sai kuwa haka ta kasance. 22Kome kuka roka cikin addu’a, in dai kun gaskanta, za ku samu.”

23Sa’adda Yesu ya shiga haikalin, sai manyan fristocin da shugabannin jama’a suka zo suka same shi yayin da yake koyarwa, suka ce, “Da wane iko kake yin wadannan abubuwa?” 24Yesu ya amsa yace masu, “Ni ma zan yi maku tambaya daya. In kun fada mani, ni ma zan fada maku ko da wane iko nake yin wadannan abubuwa.

25Daga ina baftismar Yahaya ta fito, daga sama ko kuma daga mutune?” Sai suka yi shawara a tsakanin su, suka ce, “In munce, ‘daga sama,’ zai ce mana, ‘don me bamu gaskanta dashi ba?’ 26Amma in munce, ‘daga mutune,’ muna tsoron jama’a, saboda sun san Yahaya annabi ne.” 27Sai suka amsa ma Yesu suka ce, ‘’Bamu sani ba.” Shi ma yace masu, “Nima bazan gaya maku ko da wane iko nake yin abubuwan nan ba.

28Amma me kuke tunani? Wani mutum yana da ‘ya’ya biyu. Ya je wurin na farkon yace, ‘Da, je ka kayi aiki yau a cikin gona.’ 29Yaron ya amsa yace, ‘bazan yi ba,’ amma daga baya ya canza tunaninsa ya tafi. 30Sai mutumin ya je wurin da na biyun ya fada masa abu guda. Wannan dan ya amsa ya ce, ‘zanje, baba,’ amma bai je ba.

31Wanene a cikin ‘ya’ya biyun nan yayi nufin ubansa?” Suka ce, “na farkon.” Yesu ya ce masu, “Hakika ina gaya maku, masu karbar haraji da karuwai za su shiga mulkin Allah kafin ku. 32Gama Yahaya ya zo maku a hanyar adalci, amma ba ku gaskata da shi ba, a yayinda masu karbar haraji da karuwai suka gaskata da shi. Ku kuwa, bayan kun ga abin da ya faru, baku ma tuba daga baya ba don ku gaskata da shi.

33Ku saurari wani misalin. Anyi wani mutum, mai gona. Yayi shuka a gonar, ya shinge ta, ya gina ramin matse inabi a cikin gonar, ya kuma gina wata hasumiyar tsaro, sai ya bada hayar gonar ga wadansu manoma. Sai ya tafi wata kasa. 34Da kakar inabi ta yi, sai ya aiki wadansu bayi su karbo masa amfanin gonar.

35Amma manoman suka kama bayin, suka doddoki dayan, suka kashe dayan, suka jejjefe dayan da duwatsu. 36Sai mai gonar ya sake aika wadansu bayinsa da suka fi na farko, amma manoman suka yi masu kamar yadda suka yi wa sauran. 37Bayan wannnan, sai mai gonar ya aika da dansa wurin su yana cewa, ‘za su yi wa dana biyayya.’

38Amma da manoman suka ga dan, sai suka ce a tsakanin su, ‘wannan shine magajin. Kuzo, mu kashe shi mu gaji gonar.’ 39Sai suka dauke shi, suka jefar da shi daga cikin gonar, suka kashe shi.

40To idan me gonar ya zo, me zai yiwa manoman? 41Suka ce masa, “Zai hallaka mugayen manoman nan ta hanya mai tsanani, zai kuma bada gonar haya ga wadansu manoman, mutanen da za su biya, lokacin da inabin ya nuna.”

42Yesu yace masu, “Baku taba karantawa a nassi ba,‘’ ‘Dutsen da magina suka ki ya zama dutse mafi amfani. Wannan daga Ubangijine, kuma abin mamaki ne a idanunmu?’

43Saboda haka ina gaya maku, za a karbe mulkin Allah daga wurin ku a ba wata al’umma da zata bada amfaninsa. 44Duk wanda ya fadi akan dutsen nan zai ragargaje. Amma duk wanda dutsen ya fadawa, zai nike.”

45Da manyan firistocin da farisawan suka ji wannan misalin, sai suka gane da su yake. Da suka nemi kama shi, sai suka ji tsoron taron, saboda mutanen sun dauke shi annabi.

46

Copyright information for HauULB